0
DOLE KISONI
 


DOLE KISONI


Episode 47 DOLE KISONI 

Suna shiga bayi sukazo suna zuba
musu flowers akasa wasu na
kwasan gaisuwa Aiman sakin baki
tayi dama dan sarauta ne..amma
shine mugu haka.. tadawo daga
tunanin datakene lokacin dataga wata yar dattijuwar dazata kai
kiman 55 kakkyawa da ita fara taci
gayu sosai tasa wasu kaya masu
kyalli sai murmushi take tana
karasowa ta rungume Amir shima
ya rungumeta sosai ta dago ta kalli Aiman takura mata ido saboda taga
yarinyaar na yanayi da yayanta na
Nigeria tace Amir wacece yarinyar
nan ??ya sosa keya yace mum
she is my wife dama shine surprise
din dazan baku….sai alokacin Aiman ta tuna bama ta gaishetaba
ta tsugunna har kasa tace ina
kwana mama matar tai murmushi
ta kamota ta rungume tace ya kk
zodai inkaiku wajen emir tukun
kafin mu tsaya fira…. Maman shakur


Episode  48 DOLE KISONI


 Suna shiga dakin taga daki mai
kyau an mishi ado irin ta sarauta
tahango wani dattijo kakkyawa
dan India Amir yay bala’in kama
dashi kaman yay kaki…Amir ne
taga yaje ya rungume baban yana shagwaba yace daddy i missed u
alot..baban yashafa kanshi yace i
missed u more son..Aiman har
kasa ta tsugunna tagaida mai
martaba ya amsa mata da
fara’a..Amir yace dad kun dameni nayi aure shine nai aure a Nigeria
nakawo muku ita dad yay
murmushi yace am proud of u
son..u are just lyk me wato dan na
auri mamanka yar Nigeria shine
kaima yar Nigeria ko Amir yay murmushi yace lyk father lyk son..
(iyaye mu gyara mudinga bincikan
yaranmu kan abunda suka kawo
mana..a ina kasamu??waya
baka??baso bane wai kutaso ku
baku dukan yaara ko kuma baku musu fada)
Maman shakur


Episode 49 DOLE KISONI


 Amir ne yace mum ina lil sis
simra??mum tai murmushi tace wlh
tana madrasa anma 12 zata dawo
yay murmushi yakoma kusa da
dad dinshi..ita kuma mum taja
hanun Aiman suka tafi dakinta dan taga duk bata sakeba..suka shiga
mum tace yata zauna abunki ta
zauna ita duk kunyar mum take
..mum tace saki jikinki ya sunanki?
tace Aiman imran tace Allah sarki
hakadai mum tadinga janta da hira…sai wuraren daya simra ta
dawo..ai tana ganin Amir ta gudu
taje ta rungumeshi brother nai
kewanka ya dagata sama tanata
dariya..yace kawo kunenki nafada
miki wani abu tamika mishiyace mata nakawo matata tana dakin
mum jeki gaisheta kiyita mata fira
ta sauri tace brother are serious
yace yes da gudu tayi dakin mum
dinsu
Maman shakur 


Episode 50 DOLE KISONI 


Tana shiga da gudu tafada jikin
Aiman ,Aiman harsaida ta tsorata
mum ta daka mata tsawa baki iya
gaisuwaba daga zuwa zaki haye
jikinta tana dariya tace mum i was
just so happy tace matar brother ina wuni Aiman tai mata murmushi
ta kamo hanunta tace ya kk??
simra tace matar brother wlh
kinada kyau i luv u ta rungumeta
Aiman nata dariya mum tace ya isa
rungumar kije ki chanza kayan makarantar ta wuce tana zumburo
baki…mum ta kalli Aiman tace
wanan ce kanwar Amir she is 5
now tana primary 3 ne yanzu a
madrasa izunta 15 tana hadda
Aiman nata murmushi suna cikin haka saiga simran ta shigo taja
hanunta tace matar brother zomuje
kiga dakina da toys dina takaita
dakinta tanata nuna mata
abubuwanta itadai Aiman taji tana
sonta sosai kodan ita batada kanwa ne halan ammadai tana
sonta…
Maman shakur


Episode 51 DOLE KISONI


 Sai bayan isha Amir yace ta shirya
sukoma gida simra najin haka
tadinga kuka wai wlh bazai
tafinmata da itaba yabarta anan
taje tasamu dady tana kuka dad
yace to kibisu amma ranan friday zai dawo dake saboda school kin
yarda da sauri tace eh aiko taje
taja hanun Aiman wai suje dakinta
tajada kaya suka tafi Aiman ta
tayata hada kayan itama murna
take akalla zata samu mai debe mata keya …muce ta aika maid
akirata tabar simra tatafi wajen
dakin mum..tana zuwa mum ta
miko mata wani abu a kofi kaman
madara tace yata shanye wanan
takarba tasha dan ita batasan meba…mum ta dauko wasu
abubuwa chocolate ne tabata tace
gashi kullum kidinga shan daya tai
murmushi tace nagode mum
daganan tasa ajaka mum tarakosu
har mota dad ma haka suka shiga suka tafi…sai kallonta yake amota
amma taki bari su hada ido wani
murna yake yanda bata tona mishi
asiriba suna shiga gida yana
parking suka fito taja hanun simra
sai dakinta shikuma ya tsaya dauko musu jakan simra….
Yakawo musu jakan yama Aiman
alamu da ido tazo ta murguda mai
baki ta tashi ta shiga bayi shikuma
ya wuce dakinshi da haushiiii
Maman shakur 


Episode 52 DOLE KISONI 

Washe gari bayan sunyi sallan
asuba tace ma simra jeki gaida
yayanki tako tafi shiru shiru taji
simra bata dawoba har karfe 7
shine ta sauka tana kaiwa bakin
kofan taji muryan Amir yana koyama simra karatun Al Qur’an
suratul rumm …muryarshi dadi
kaman na sudaies mamakine ya
cika mata ciki dama mutumin nan
nada ilimin addini yake iskanshi da
neman mata haka motsin dataji za’a bude kofan ne yasa tai maza
tajuya ta wayance kaman tana
neman abu simra takarso tace
matar brother mekikeyi anan??
tace bakomi tajata suka shiga
kitchen ta dafa musu egg pizza da hot tea kamshi duk ya cika gidan
suna cikin ci a dining Amir yafito
yataho ya zauna kusa da ita yace
baby ina nawa ta daure fuska
kawai gani tayi yasa hannu yafara
cin nata simra tace brother karka cinye mata mana ya daure fuska
taja bakinta tai shiru saida yaci
yay nak sanan ya mike ya manna
mata kiss abaki yace baby natafi
clinic take care jitayi kaman ta
kasheshi tai banza dashi shikuma yawuce yatafi…
Maman shakur 



Episode 53 DOLE KISONI 


Haka suka cigaba da rayuwa
simra nadebe ma Aiman kewan
iyayenta sosai tana bala’in son
yarinyar dan tanada shiga rai ga
surutu daban dariya yayinda Amir
najin dadin yanda tarage damuwa.. yanzu kullum da safe sai ya cinye
mata abincin yana jin dadin girkinta
sosai saida yanzu ko kallo bai
ishetaba dan kullum kara tsanarshi
takeyi..
******yaune takama friday randa simra zata tafi tun safe Aiman take
kuka amma a boye dan batason
simra tagane tai wani zuru zuru
yanda Amir yaga tayi yasa tabashi
tausayi yaki kaita harsai karfe 3 da
dady yakira yace yadawo da simra shine yaje yace tafito Aiman kuka
take sosai itama simra kuka da
kyar ya babbare simra daga jikin
Aiman yasata amota itakuma
Aiman takoma daki tana kuka daga
baya tamike tai wanka tasa wani three quarter iya guiwa yakamata
sosai dawata yar shimi mai v neck
shima yakamata tazauna tai shiru
har karfe biyar..tana zaune kawai
taji tana sha’awan zuwa tsakar
gida tako fito tana fitowa kawai ta hango gate abude kuma ba
securities din dukansu basa wurin
ai batai tunanin kayan dake
jikintaba da gudu tayi gate tafita
daga gidan gudu take iya karfinta



Episode 54 DOLE KISONI


 Amir natare da dad dinshi suna fira
yana tambayarshi ya Aiman??yace
tana lpy dad hakadai sunata firan
da da uba kawai jiyayi kirjinshi ya
buga dummm saikuma yaji
zuciyarshi na Aiman Aiman kawai mikewa yayi zumbur yay ma baban
nashi sallama dad yana ka tsaya
kayi mangariva mana yace dad
zandan leka clinic ne yace to bye
yama mum sallama da simra yatafi
gudu kawai yake yana zuwa dakin Aiman ya shiga straight yaga bata
ciki yaduba bayi bata ciki yakoma
kitchen yatambayai kuku tace dazu
around 5 taga tafito tsakar gida
daganan bata kara ganintaba ..duk
ya rude yatafi wajen securities yace musu Aiman ta fita sukace
a’a sai daya daga cikinsu yace
kodai dazu damukaje taya
neighbours dinmu kashe snake ne
tafita Amir yace wot??kun fita
dukanku yace shikenan yarinyar mutane ta gudu yace kuje
kunemota inba hakaba nakoreku
duka da sauri yakoma mota yaja
aguje yafita kaman mahaukaci…
Maman shakur 


Episode 55 DOLE KISONI


 Aiman bata daina guduba saida
taga tabar unguwan kwata kwata
addu’a take Allah ya taimaketa
tasamu wanda zai bata kudin jirgi
takoma Nigeria tanata tafiya da
sauri sauri…. Amir yay nema harya gaji
anguwan dasuke jere dasu yake
shiga daya bayan daya yana
dubawa amma bai gantaba Addu’a
yake Allah yasa yaganta bayason
tafada wani halin kuma dan yasan akwai yan iska sosai a India harda
hawayenshi duk ya rude …
Aiman tana cikin saurinta dan 7 ma
yayi ta hango wasu samari su 3
akofar wani gida ahankali takarasa
wajensu ta tsugunna har kasa tana dan Allah kutaimakamin da
kudin jirgi nakoma garinmu harda
kuka suko ido kawai suka zuba
mata sunga yarinya kakkyawa ga
gashi ga diri suka kalli juna sukai
magana da India sanan suka juyo suka kalleta daya daga cikinsu
yace indai kudin jirgi kikeso zamu
baki amma saidai ki shigo dakinmu
ki amsa ba anan ba da sauri ta
kallesu tace nidai bazan shiga
dakin mazaba ku barshi nama fasa ta mike zata tafi kawai taji sun
kamota tana ihu kusakeni dan
Allah karku rabani da mutuncina
kusakeni…
Maman shakur

Post a Comment

 
Top